AISHATUL HUMAIRAH
https://whatsapp.com/channel/0029Vanj1jbDjiOjXkiile2rz
Follow My WhatsApp channel
Follow my WhatsApp group
https://chat.whatsapp.com/IIKzwCAJAd61b7Ngw763L9
AISHATUL___HUMAIRAH
..... Labarin Indo .....
❤️π❤️π❤️π❤️π❤️π❤️
=Na=
WALEEDAH MUHAMMAD
(AUNTYNMU)
ππ·πΈπ·ππ·πΈπ·ππ·πΈπ·ππ·πΈπ·π
The Story of life childhood, Entertainment, And Love.
. SADAUKARWA GA YAN UWANA.
Kauyen wakaza dake garin dustinma karkashin katsina state, a yau kuma can naje domin dakko muku wani muhimmun labari, ku biyoni dan jin ina zamu kwana, mai rubutu taku MATAR UNCLE.
KAUYEN WAKAZA
KATSINA STATE
πΊ1&2πΊ
Tafe take rungume da allo a hannunta, da ka ganta kasan daga makaranta ta dawo,cikin tsakar rana take tafiya yayin da kafarta ko takalmi babu, tayi wani bututu da jikinta,can nesa kadan naga tana wangale baki tare da bude baki tana fadin "Salame Salame, wadda aka kira da wannan sunan ne naga ta juyo take ta zuba na kare.
Ganin ta fara gudu ne yasa yarinyar binta, cikin lokaci kankane ta kamota tare da bugata da kasa, ta kuma haye kan ruwan cikinta, tana zuba mata kasa a baki, can kuma ta saki dariya tace "wai da ke salame kinci bati kenan ko, har ni zaki sa malam Dahe ya dakeni ko,tashi tayi daga kanta bayan ta cika bakin da kasa, ga jini yana zuba ta hancinta amma bata raga mata ba, bishiyar darbejiyan dake wajen tai tsalle ta dane tare da fizgota, lokaci guda ta dawo hannunta, bata wani ji tausayinta ba ta fara zabga mata, salame ba damar ihu.
Dik yawan mutanen da suka taru an kasa samun wani yayi mata magana, domin kana mata magana kanka zata dawo, kamar daga sama taji wata murya, lokaci guda ta yarda bulalan, tana kallonsa cike da tsantsar tsoro,wani saurayi ne cike da karfi ya fara jan hannunta suka bar wajen cikin lokaci kankane, mutanen dake wajen ne suka kama salame ta mike daganan kuma kowa ya watse ya kama gabansa.
Tafiya suke a daidai lokacin suka shiga cikin wani gida, na jar kasa ne, shigarsu ke da wuya na hangi wasu bukkoki guda 3 da suke a jere sai daga baya can na hangi wani abu kamar rumbu. Shigowarsa ne ya kalli tsohuwar dake gidan tana kokarin hada itace, domin ta dora sanwar abincinta, juyowar da zatayi ne ta ga mutum tare da yarinya, cikin hausanta irin ta fulani tace "to garba kace yarinyar yau ma tayi halin nata, kallon yarinyar tayi tace" wai ke indo yaushe zakiyi hankali ne iye, ke gaba daya bakya girma, rigima yau daban ta gobe daban, kafin ta rufe bakinta aka rangwada sallama a kofar gidan,garba ne yaja tsaki sannan ya saketa ya fita dan yasan kiran mai gari ne.
Fitarsa ne yasa indo ta kalli tsohuwar tace "to ke kuma ina ruwanki, mata sai sa'idon jaraba, malama ki kyaleni naci zamani na, ke wayasan ma me kikayi da kika tashi yin taki kuruciyar, kawai dan nazo a hannunki shikenan sai ki fara min jaraba, na rantse da allah kuma kema kin jawa kanki, a lokacin data rufe baki ne muryar garba ta fara tashi, alamun shigowar sa kenan,"zaki tashi mu wuce wajen mai gari ko sai na bata miki, yarinya mara mutunci, narantse da allah muka dawo daga wajen mai gari inaga sai na targadaki tsaki yaja ya tashi yayi waje, ba shiri ta tashi ta bishi tana kunkuni kamar wani sa'anta.
Iyalle bayan fitarta kuwa rike baki tayi tana fadin "kai wannan yarinya allah ubangiji ya shiryeki, yarinya karama sai wulakanci da rashin kunya, ga shegiyar fitsara, yarinyar kamar yarinyar aljanu, mayafinta dake jikin igiya taja sannan ta fice ta nufi wajen mai gari dan jin ina za a kwana a wannan lamari na indo.
A wajen mai gari kuwa, salame ce da mahaifiyarta sai mahaifinta a zaune a wajen mai gari, yayin da kallo daya zakayi mata kasan ta daku ba karya, shigowar indo da garba ne yasa taja tsaki, kallonta indo tayi take a wajen ta fara babbaka dariya kamar wata sabon kamu,dik yawan mutanen wajen sakin baki sukayi suna kallonta kamar wata sabuwar kamu, tsawar da garba ya daka mata ne yasa ta yin shiru, salame ta kalleta cike da kuluwa, mai gari sanin halin indo ne yasashi fara magana a hankali.
"ke indo me ya hadaki da salame ne, cike da tsiwa tace" yo baba me gari kaji min wani batu dana kasa gane ina ka dosa, salame ce a makarantar kan tudu tasa malam iliya dan me karfi ya dakeni, ni kuma wallahi tinda ya dakeni nace a kanta zan rama, shisa na kamata na jibgi abar banza, mai gari ne yayi gyaran murya yace "ke bakisan a inda kike ba har kike wannan lafazin, kallon salame yayi yace ke salame meyasa kikasa malam ya daketa.
Cikin kuka da sharbar majina, salame tace" baba mai gari wallahi ita ce ta samu allo na ta wanke min hi a kogin dan marka dayake kan hanya, shi ne ni kuma da muka je makaranta na fadawa malam, yace sai ta bada kudi an min wani rubuta, da tace bazata biya ba shine yayi mata bulala goma, sannan yace ta bani hakuri amma sai taki.
Mai gari ne ya kalli indo yace ke indo haka akayi"dariya ta kyalkyale da ita tace eaa haka akayi mana mai garin garinmu.
Mai gari ne yayi nuni take wani dogari ya fito da wata zabgegiyar dorina mai baki biyu, indo idanunta idan dorina ai tini ta tattara ya nata ya nata tai waje ta bar wajen, yayin da mai gari yace a bita a kamota dik inda taje.
Gudu take suna binta, ta kasuwar garin ta biyo, tana yi tana waiwaye, a lokaci daya ta bace musu, sunyi nema sunyi nema har sun gaji abin har ba'a magana, haka suka hakura suka dawo domin fadawa mai gari.
Indo kuwa samu tayi ta shiga rumfar idi mai shayi cikin inda ake ajiye bread nan ta samu ta rakube, idi shi tsoransa allah kada ma ta dauki wani abun, sai da ta dauki wajen mint 30 sannan ta fito, a lokacin rana ta take, kallon biredin idi tayi ta hadiye yawu, kallonsa tayi tana daukar daya, cike da bacin rai idi yace ke wallahi ajiye min biredi tinda ba ubanki bane ya siya min, wani kallo tsyi masa kallon baka da wayo, tare da fadin zo ka kwata, nufota yayi cikin sa'a kuwa ta tsugunna kasa ta debo ta watsa masa a ido,ta runtua na kare.
Tafiya take tana yagar biredin dake hannunta, a lokaci guda ta cinye hade da sakin wata gyatsa, shafa cikin tayi sannan ta fara magana, amma gaskiya ban koshi ba, kuma ni bazan koma wannan gidan ba indai garba baya nan, kara na bari sai can anjima, tafiya take tana watsa kasa, can gaba kadan tazo shigewa ta hango tukunya a wani gida, murmushi ta saki tana dariya, shiga tayi tana zazzare idanu,
Faranti ta hango da ludayi hakan yasa ta bude tukunyar, dafaffiyar shinkafa ce jellof taji alayyahu da manja, diba tayi sannan ta koma gefe ta fara ci hankali kwance, har ta gama cinyewa tasha ruwa sannan taji alamun mutum zai fito, da gudu ta fice daga gidan tana waiwaye.
Haka tai ta gantali a cikin kauyen wakaza ganin dare yakiyi ne yasa ta tafiya gonar wuro tare da danewa bishiya, can kusan la'asar sannan ta sakko tai hanyar rafi.
Sai can wajen magariba sannan ta fara kokarin shiga gidan nasu, ba kowa a tsakar gidan hakan yasa fa shige madafa, tuwon da iyalle ta gama ta kwasa ta fara ci kamar jaka, sannan ta shige makewayi daga baya kuma ta fito, a dai dai lokacin iyalle tafito, kallon ta take cike da mamaki, "ke yanzu indo haka kika zaba ko, wallahi ke da mai gari domin yanzun nan zan kira garba yazo yayi miki maganin abinda yake damunki, yarinya sai iskanci, murguda baki indo tayi" ke wallahi iyalle kin cika jaraba, kin san allah kika sake kika kira garba wallahi ai bata rufe bakinta ba taji shigowarsa, kallin kallo aka fara, a wani gudu tai tsalle ta dare katangar gidan ta gudu.
Sai wajen 10 ta dawo daga dandali a lokacin bakajin sautin komai sai na tsuntsaye,mainakon tayo hanyar gida sai tayi hanyar gidsn mai gari, cikin sa'a kuwa fa dare katangar gidsn ta fada cikin gidan, turakar mai gari ta karasa, sai kuma ta juyo ta dawo zuwa tsakar gidan, wani mulmulallen icce ta dauko tare da burshi ne fuskarta da toka kamar fatalwa,dakin mai gari ta shiga shi kuwa sai shara bacci yake, kamar xaga sama ta daga wannan iccen ta rabka masa a kafa, a fisrgice ya tashi zaune yana fadin nashiga3, fitilar gefe ta kunna a lokacin ya ganta fara fat abinka da me bacci.